DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima zai wakilci shugaba Tinubu a kasar Senegal wajen bikin cika shekara 65 da samun ‘yancin kan kasar

-

Kashim Shettima

 Mataimakin shugaban kasar Shettima ya bar Abuja ne zuwa Dakar domin ya wakilci shugaba Tinubu a wajen bikin cikar Senegal shekaru 65 da samun ‘yancin kai.

Kasar Senegal na bikin ranar samun ‘yancin kai a ranar 4 ga watan Afrilun kowace shekara, inda ake bikin ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Faransa a shekara ta 1960.

Google search engine

Ranar dai ta kasance cikin alfahari da al’ummar kasar, tare da shagulgula, da yin fareti da wasanni na al’adun kasar.

Halartar mataimakin shugaban kasa a taron na shekara-shekara, don girmama goron gayyatar da shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye ya yi wa shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya biyo bayan kyakkyawar alakar da ke tsakanin Nijeriya da Senegal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara