DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya cusa kabilarsa a sabbin nade-naden kamfanin NNPCL – Kungiyar Malam Shekarau ta LND

-

Malam Ibrahim Shekarau

Google search engine

Kungiyar League of Northern Democrats (LND) ta Malam Ibrahim Shekarau ta zargi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da fifita wata kabila a kan sauran kabilun Nijeriya wajen nade-naden mukamai a gwamnati.

Kungiyar a sanarwar da mai magana da yawunta Dr. Ladan Salihu ya fitar, ta buga misali da yadda rabon mukamai na baya-bayan nan da shugaban kasa ya yi a Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) ya fi bayar da fifiko ga wata kabila fiye da sauran kabilun kasar.

LND ta ce ta san da cewa dokokin Nijeriya sun amince wa shugaban kasa ya yi sauye-sauye amma ta ce wannan mataki na fifita kabilarsa a kan sauran kabilun kasar  ba daidai ba ne, kuma kungiyar ba za ta goyi bayan hakan ba, domin hakan tauye adalci da ka’idojin daidaito a raba mukaman gwamnati ne karara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara