DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya cusa kabilarsa a sabbin nade-naden kamfanin NNPCL – Kungiyar Malam Shekarau ta LND

-

Malam Ibrahim Shekarau

Google search engine

Kungiyar League of Northern Democrats (LND) ta Malam Ibrahim Shekarau ta zargi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da fifita wata kabila a kan sauran kabilun Nijeriya wajen nade-naden mukamai a gwamnati.

Kungiyar a sanarwar da mai magana da yawunta Dr. Ladan Salihu ya fitar, ta buga misali da yadda rabon mukamai na baya-bayan nan da shugaban kasa ya yi a Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) ya fi bayar da fifiko ga wata kabila fiye da sauran kabilun kasar.

LND ta ce ta san da cewa dokokin Nijeriya sun amince wa shugaban kasa ya yi sauye-sauye amma ta ce wannan mataki na fifita kabilarsa a kan sauran kabilun kasar  ba daidai ba ne, kuma kungiyar ba za ta goyi bayan hakan ba, domin hakan tauye adalci da ka’idojin daidaito a raba mukaman gwamnati ne karara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Adams Oshiomhole ya buƙaci gwamnatin Tinubu ta garƙame duk wanda ya ƙi biyan haraji

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

‘Yan APC kawai jam’iyyar za ta ba mukamai bayan zaben 2027 – Nentawe Yilwatda

Shugaban jam'iyyar APC na Nijeriya Farfesa Nentawe Yilwatda ya bayyana cewa ba za su bai wa duk wanda ba dan jam’iyya mukami ba bayan zaben...

Mafi Shahara