DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fadar shugaban kasa ta ƙaryata zargin aikata ba daidai ba wajen ba da mukaman gwamnati kamar yadda ake yaɗawa

-

A cikin wata sanarwa da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (OSGF) ya fitar, gwamnatin ta ce tana bin tanadin kundin tsarin mulkin kasa na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwanskwarima) musamman sashen 14, wajen tabbatar da adalci da wakilci daga dukkan yankuna.
Sanarwar ta ce Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, na da cikakken burin hadin kan kasa, kuma yana yin nade-nade ne bisa tushen gaskiya, adalci da ga kowa da kowa.
Ofishin sakataren gwamnatin ya bukaci jama’a da su yi watsi da jita-jitar da ba su da tushe, tare da shawartar su da su dinga dogaro da hanyoyin sadarwa na hukuma wajen samun sahihan bayanai.
A karshe, sanarwar ta gargadi masu yada kalaman rarrabuwar kai da zargin da ba su da tabbas da su daina, domin hakan ba zai amfani kasar nan ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun raba Naira biliyan 116.4 ga ɗalibai sama da dubu 624 – Asusun NELFUND

Asusun ba da bashin karatu ga ɗaliban manyan makarantu ya bayyana cewa ya raba Naira biliyan 116.4 ga ɗalibai sama da dubu 624, tun bayan...

Tsohon kwamishinan Ganduje ya soki gwamnatin Abba bisa zargin sayar da filin makarantar

Tsohon kwamishinan ilimi na a zamanin Ganduje, Muhammad Sanusi Sa'id Kiru, ya soki matakin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da Makarantar Sakandare ta ‘Yan...

Mafi Shahara