DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jigo a jam’iyyar PDP Bode George ya ce shugaban riko na Rivers bai da hurumin naɗa muƙamai

-

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Olabode George, ya gargadi shugaban riko na jihar Ribas, Admiral Ibok-Ete Ibas mai ritaya, kan nade-naden da yake yi a kwanan nan da kuma sake fasalin hukumomin jihar.
Bode George ya bayyana hakan a matsayin abinda ya saba doka da kuma yiwuwar yin da na sani a gaba. 
Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar da aya fitar yau Jumu’a, inda ya bukaci Ibas da ya mutunta kundin tsarin mulki da bin doka da oda. 
Jigon na PDP ya kuma yi soka kan shugabannin rikon kwarya na kananan hukumomi 23 da ya naɗa, duk kuwa da umarnin da kotu ta bayar na haramta irin wadannan ayyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara