DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku Abubakar: Ziyarar gaisuwar sallah muka kai wa Buhari, ba siyasa ba

-

Madugun adawar siyasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa ziyarar da ya kai wa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a Kaduna ba ta da alaka da wata tattaunawa ko hadakar siyasa da ke da nasaba da zaben 2027.

Google search engine

Atiku, wanda ya jagoranci wasu fitattun ’yan siyasa ciki har da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Tambuwal, ya ce sun kai wa Buhari ziyara ne domin gaisuwar Sallah da sada zumunci. Ya kara da cewa, bayan ya kammala ayyukansa na Sallah a Adamawa, ya samu zarafin kai wa tsohon shugaban kasar ziyara.

Ziyarar na zuwa ne kwanaki biyu bayan gwamnonin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Sanata Hope Uzodimma su ma suka kai irin wannan ziyarar gaisuwa ga Buhari. Wannan ya kara janyo ce-ce-ku-ce a fagen siyasa musamman kan makomar zabubbuka masu zuwa, amma Atiku ya jaddada cewa tafiyarsu ba siyasa ba ce.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara