DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya na shirin samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 8,000 nan da shekarar 2027

-

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirin samar da wutar lantarki a kalla megawatt 8,000 a karshen wa’adin mulkin shugaba Bola Ahmed Tinubu na farko a shekarar 2027.

Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a yayin taron manema labarai karo na shida a 2025 a Abuja.

Adelabu ya ce abin da aka sa a gaba ya tabbata, yana mai cewa tuni fannin samar da wutar lantarki ya samu ci gaba da kashi 40 cikin 100 tun bayan hawan gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu.

Ministan ya ce ya bibiyi tarihin yadda ake samar da wutar lantarki a Nijeriya, inda ya bayyana cewa an dauki kusan shekaru 40 – daga 1984 zuwa 2022 – ana samun megawatt 2,000 zuwa 4,000 amma nan da karshen wa’adin mulkinsu za a samu megawatt 8000.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara