Gwamnatin mulkin sojan Burkina Faso ta ce ta dakile wani yunkuri na hambarar da gwamnatin shugaban mulkin sojan kasar, Kyaftin Ibrahim Traoré, wanda suka yi zargin hannun wasu dake neman mafaka makwabciyar kasar Ivory Coast.
Ministan tsaron kasar Mahamadou Sana, ya ce tsofaffin soji da wadanda ke aiki ne suka shirya juyin mulkin, ta hanyar kai wa fadar shugaban kasa hari ne a makon jiya.
Tun shekara ta 2022 da shugaban mulkin sojan Kyaftin Ibrahim Traoré ya kwace mulki ta hanyar juyin mulki ake kokarin hambarar da shi.