DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An tsare wasu jami’an hukumar Civil Defence bisa zargin tatsar kudade a hannun jama’a da suka kai Naira miliyan 5.2

-

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Nijeriya ta bayar da umarnin tsare wasu jami’an da ake zargin suna da hannu wajen karbar naira miliyan 5.2 daga hannun wani matafiyi, biyo bayan umarnin da ministan harkokin cikin gida, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo ya bayar.

Umurnin na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun hukumar NSCDC, Afolabi Babawale, a ranar Laraba.

Google search engine

Lamarin wanda ya dauki hankulan jama’a a shafukan sada zumunta, an ruwaito jami’an na karbar kudin ne daga hannun wani matashi da ya taso daga Ado-Ekiti a jihar Ekiti zuwa Akure, jihar Ondo.

A matakin da ya dauka, kwamandan rundunar, Ahmed Audi, ya yi Allah wadai da halayyar da jami’an suka nuna, abin da ya bayyana rashin da’a da kuma saba wa ka’idar aiki da hukumar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara