DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An ji karar harbe-harbe a wurin taron magoya bayan Wike a jihar Bayelsa

-

An shiga cikin tashin hankali a birnin Yenagoa ta jihar Bayelsa, bisa karar harbe-harbe da aka ji a wurin masu biyayya ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike karkashin wata kungiya mai suna NEW Associates.

Kungiyar ta shirya taron ne karkashin jagorancin George Turnah, jigo a jam’iyyar PDP a jihar.

Ana ci gaba da gudanar da taron ne a lokacin da aka yi ta jin karar harbe-harbe a yankin, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.

Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan harbe-harbe, sakataren kungiyar NEW Associates a jihar Bayelsa, Comrade Ebilade Ekerefe, ya ce za su ci gaba da gudanar da taron.

A halin yanzu, magoya bayan NEW Associates sun sake haduwa don ci gaba da gangamin taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara