DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a yi wa matasan NYSC karin kashi 100 na alawus a jihar Zamfara

-

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal na ya ba da umarnin kara yawan alawus-alawus na matasa masu yi wa kasa hidima, NYSC, da za su yi aiki a jihar da kashi 100 cikin 100.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a Gusau, yayin da yake bude sansanin masu yi wa kasa hidima Batch ‘A’ na 2025 a jihar.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Abubakar Nakwada a wajen taron, ya nanata kudirin gwamnatinsa na tabbatar da tsaro da jin dadin daukacin mambobin su 550 da aka tura jihar.

A wajen taro ya sanar da cewa an bayar da umarnin a dawo da biyan alawus-alawus tare da karin wani kaso ga duk masu yi wa kasa hidima da ke jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara