DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Nasir Idris na Kebbi ya nesanta kansa daga jita-jitar ficewa daga jam’iyyar APC

-

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya nesanta kansa daga rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa shi da wasu gwamnoni hudu na shirin ficewa daga jam’iyyar APC don shiga wata hadaka da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da wasu ‘yan siyasa ke kokarin kafawa.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ahmed Idris, ya fitar, Gwamna Idris ya bayyana rahotannin a matsayin karya, da kuma kage, inda ya tabbatar da cewa shi ba dan siyasa ne mai yawo daga jam’iyya zuwa jam’iyya ba.

Gwamnan ya ce “Ina da tushe a APC, ‘jam’iyyar APC ce ta daga ni, kuma ina wa APC hidima,” yana mai jaddada cewa ko da kowa zai fice a jam’iyyar APC, shi ne zai zama na karshe da zai bar jam’iyyar da ta gina shi.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara