Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya nesanta kansa daga rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa shi da wasu gwamnoni hudu na shirin ficewa daga jam’iyyar APC don shiga wata hadaka da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da wasu ‘yan siyasa ke kokarin kafawa.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ahmed Idris, ya fitar, Gwamna Idris ya bayyana rahotannin a matsayin karya, da kuma kage, inda ya tabbatar da cewa shi ba dan siyasa ne mai yawo daga jam’iyya zuwa jam’iyya ba.
Gwamnan ya ce “Ina da tushe a APC, ‘jam’iyyar APC ce ta daga ni, kuma ina wa APC hidima,” yana mai jaddada cewa ko da kowa zai fice a jam’iyyar APC, shi ne zai zama na karshe da zai bar jam’iyyar da ta gina shi.