DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dole mu sake ba Tinubu dama a 2027 ya karasa aikin da ya dauko – Minista Festus Keyamo

-

 

Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya bukaci ‘yan jam’iyyar APC da su manta da bambancin ra’ayi da son zuciya, su marawa shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin sake samun nasara a zaben shekarar 2027.

Google search engine

 

                                   Festus Keyamo

Keyamo ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da tashar Channels Television a ranar Litinin, inda ya jaddada cewa dole ne a sake zaɓen Tinubu domin ya kammala sauye-sauyen da ya fara a harkokin mulki da tattalin arziki.

A cewar Ministan, nasarar cigaba da aiwatar da sauye-sauyen na bukatar hadin kai da fahimtar juna daga cikin jam’iyyar, tare da dagewa wajen tabbatar da dorewar ayyukan da aka rigaya aka fara.

Festus Keyamo, ya bayyana dalilin da ya sa ya mika shugabancin tsarin jam’iyyar APC ga Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, wanda kwanan nan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar mai Mulki, inda yace ya zama wajibi a hada kai da karfafa gwiwar sabbin ‘yan jam’iyyar da suka dawo domin ci gaban jam’iyyar a matakin jiha da kasa baki daya kafin tafiyar ta kai gacci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara