DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wajibi a sauya yadda ake juya jam’iyyun siyasa a Nijeriya – Abbas Tajudden

-

Kakakin Majalisar Wakilai ta Tarayya, Hon. Tajudeen Abbas, ya bukaci a inganta tsarin jam’iyyu a Najeriya domin su daina zama tamkar kamfanonin kasuwanci da shugabanninsu ke amfani da su don ribar kansu.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN yace taron bitar wanda ya gudana a Abuja kan kudirin dokar gyaran jam’iyyu, Cibiyar bada taimakon Zabe ta Turai (ECES) ce ta shirya tare da hadin gwiwar YIAGA Africa da Cibiyar Kukah, Abbas – wanda Hon. Ishaya Lalu ya wakilta – ya ce dole ne a kara kaimi wajen sanya jam’iyyu su rika aiki da tsari da manufa.

Ya ce, duk da cewa Najeriya na bin tsarin mulkin shugabanci irin na Amurka, akwai tazara mai girman gaske wajen yadda ake rajista da kaka-gida da masu kudi kanyi wajen zuba jari a harkokin jam’iyyu.

Kakakin majalisar ya nuna damuwa da yadda yawancin jam’iyyun Najeriya ke fama da rashin tsari da akida, wanda hakan ke haddasa sauya sheka da karancin amincewar jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara