Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya bukaci ‘yan jam’iyyar APC da su manta da bambancin ra’ayi da son zuciya, su marawa shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin sake samun nasara a zaben shekarar 2027.
Festus Keyamo
Keyamo ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da tashar Channels Television a ranar Litinin, inda ya jaddada cewa dole ne a sake zaɓen Tinubu domin ya kammala sauye-sauyen da ya fara a harkokin mulki da tattalin arziki.
A cewar Ministan, nasarar cigaba da aiwatar da sauye-sauyen na bukatar hadin kai da fahimtar juna daga cikin jam’iyyar, tare da dagewa wajen tabbatar da dorewar ayyukan da aka rigaya aka fara.
Festus Keyamo, ya bayyana dalilin da ya sa ya mika shugabancin tsarin jam’iyyar APC ga Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, wanda kwanan nan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar mai Mulki, inda yace ya zama wajibi a hada kai da karfafa gwiwar sabbin ‘yan jam’iyyar da suka dawo domin ci gaban jam’iyyar a matakin jiha da kasa baki daya kafin tafiyar ta kai gacci.