DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu inda aka yi son-rai wajen zaben jami’an da za su yi wa alhazai hidima a hajjin 2025 – NAHCON

-

Hukumar kula da hajji ta Nijeriya NAHCON ta nesanta kanta daga zargin cin hanci da rashawa a cikin tsarin zaben tawagar likitocin da za ta kula da masu aikin hajji na shekarar 2025.

Jaridar Daily Nigerian ta ba da labarin cewar ana zargin NAHCON da yin wata kumbiya-kumbiya wajen zaben ma’aikatan wucin gadi da za a tura Saudiyya don aikin Hajjin bana.

Google search engine

Sai dai hukumar, cikin wata sanarwa da Shafii Sani-Mohammed ya sanya wa hannu, jami’in yada labarai a hukumar, ta musanta aikata duk wani ba daidai ba da ake zargi, tana mai jaddada cewa ana gudanar da aikin ne karkashin wani kwamiti na musamman wanda manyan jagororinsa suka fito daga kwararri a fannin lafiya, ba na hukumar NAHCON ba.

muhammad kabir
muhammad kabirhttp://dclhausa.com
Muhammad Kabir, ƙwararren ɗan jarida ne wanda ke da gogewa a fannin yada labarai na zamani (Digital Media)...

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara