DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin PDP sun cimma matsaya da Wike don ceto jam’iyyar kafin zaben 2027

-

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun tabbatar da cewa akwai sabuwar yarjejeniya tsakanin wasu gwamnonin jam’iyyar PDP da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, da nufin kawo zaman lafiya da hadin kai cikin jam’iyyar kafin babban zaben shugaban kasa na 2027.

Wani babban jigo daga cikin jam’iyyar ya shaida wa Sunday Punch cewa Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ne ya wakilci gwamnonin PDP a wani muhimmin zama da suka yi da Wike a birnin Legas makon jiya.

Majiyar ta bayyana cewa taron ya maida hankali ne kan rikicin siyasa da ke faruwa a jihar Ribas tsakanin Wike da gwamnan da aka dakatar Siminalayi Fubara. Haka kuma sun tattauna batutuwan shugabancin yankin Kudu maso Kudu na jam’iyyar da kuma mukamin Sakataren jam’iyya na kasa da har yanzu ba a warware ba tun Disambar 2024.

Jam’iyyar PDP dai tana fama da rikice-rikice na cikin gida tun bayan kammala zaben 2023, kuma yunkurin sulhu da kwamitocin jam’iyyar – ciki har da NWC, BOT, NEC da kuma Gwamnonin PDP – suka yi, ya ci tura, maimakon magance matsalolin sai kara rura wutar rikici.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara