DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisar wakilai 8 na LP da PDP sun sauya sheka a jihohin Delta da Enugu

-

A ranar Talata ‘yan majalisar wakilai takwas suka bayyana ficewa daga jam’iyyunsu zuwa wasu jam’iyyu daban-daban.

‘Yan majalisar wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC, yayin da ‘yan majalisa biyu daga jihar Enugu suka bar jam’iyyar Labour suka koma PDP.

Google search engine

A yayin zaman majalisar na yau talata ne aka karanta sanarwar ficewar ‘yan majalisar.

Wadanda suka sauya sheka daga jihar Delta sun hada da Nicholas Mutu Bomadi da Nnamdi Ezechi, Jonathan Okodiko, Thomas Eriyetomi, Julius Pondi, da kuma Victor Nwokolo.

‘Yan jam’iyyar Labour da suka koma PDP sun hada da Mark Obetta daga Enugu da Dennis Agbo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara