DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisar wakilai 8 na LP da PDP sun sauya sheka a jihohin Delta da Enugu

-

A ranar Talata ‘yan majalisar wakilai takwas suka bayyana ficewa daga jam’iyyunsu zuwa wasu jam’iyyu daban-daban.

‘Yan majalisar wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC, yayin da ‘yan majalisa biyu daga jihar Enugu suka bar jam’iyyar Labour suka koma PDP.

A yayin zaman majalisar na yau talata ne aka karanta sanarwar ficewar ‘yan majalisar.

Wadanda suka sauya sheka daga jihar Delta sun hada da Nicholas Mutu Bomadi da Nnamdi Ezechi, Jonathan Okodiko, Thomas Eriyetomi, Julius Pondi, da kuma Victor Nwokolo.

‘Yan jam’iyyar Labour da suka koma PDP sun hada da Mark Obetta daga Enugu da Dennis Agbo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara