Wani matashi É—an shekara 18, da aka tura don koyon sana’a a jihar Anambra, ya shiga hannun hukuma bayan zargin dirkawa mata 10 ciki a watanni biyar kacal, wanda ya haÉ—a da ‘yar ubangidansa da abokiyar zamansa a shagon sana’ar.
Kwamishinar Mata da Jin Daɗin Jama’a ta jihar Anambra, Ify Obinabo, ta bayyana hakan a wani faifan bidiyo da ta watsa kai tsaye a kafar sada zumunta a ranar Laraba, lamarin ya faro ne tun bayan da aka tura matashin zuwa koyon sana’a.
Bayan wata uku kacal da fara koyon sana’ar, matashin ya ke bibiyar ‘yar maigidansa da kuma wata zaman shago, lamarin da ya sa aka kori shi daga wurin koyon sana’ar.
Bayan ya koma gari, Kwamishina Obinabo ta ce lamarin ya kara ta’azzara, inda tace uwar yaron ce ta zo ofishinta don neman mafita.
Obinabo ta bayyana cewa bata iya magance lamarin ita kadai ba, ta kuma nemi shawarwari daga jama’a don gano mafita – tana tambayar ko akwai wani al’amari na ruhanai da ke tattare da lamarin.