DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yaron shago ya yi wa ‘yan mata 10 ciki, daga cikinsu hada diyar ogansa a Anambra

-

Wani matashi É—an shekara 18, da aka tura don koyon sana’a a jihar Anambra, ya shiga hannun hukuma bayan zargin dirkawa mata 10 ciki a watanni biyar kacal, wanda ya haÉ—a da ‘yar ubangidansa da abokiyar zamansa a shagon sana’ar.

Kwamishinar Mata da Jin Daɗin Jama’a ta jihar Anambra, Ify Obinabo, ta bayyana hakan a wani faifan bidiyo da ta watsa kai tsaye a kafar sada zumunta a ranar Laraba, lamarin ya faro ne tun bayan da aka tura matashin zuwa koyon sana’a.

Bayan wata uku kacal da fara koyon sana’ar, matashin ya ke bibiyar ‘yar maigidansa da kuma wata zaman shago, lamarin da ya sa aka kori shi daga wurin koyon sana’ar.

Bayan ya koma gari, Kwamishina Obinabo ta ce lamarin ya kara ta’azzara, inda tace uwar yaron ce ta zo ofishinta don neman mafita.

Obinabo ta bayyana cewa bata iya magance lamarin ita kadai ba, ta kuma nemi shawarwari daga jama’a don gano mafita – tana tambayar ko akwai wani al’amari na ruhanai da ke tattare da lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara