DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu karɓi Kwankwaso idan ya yanke shawarar koma wa APC- Ganduje

-

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta karɓi tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, idan har ya yanke shawarar dawowa jam’iyyar.

Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da Ministan Jiha na Ma’aikatar Gidaje da Cigaban Birane, Hon. Yusuf Ibrahim Atah, ya kai masa ziyarar ban girma a hedikwatar APC da ke Abuja.

Google search engine

Ya ce, idan mutum yana neman mafaka daga gida guda, wajibi ne a buɗe masa ƙofa, musamman idan akwai dangantaka ta siyasa da tarihi tsakaninsu.

A baya -bayan nan rahotanni sun nuna cewa jam’iyyar APC na ci gaba da karɓar sabbin mambobi daga sauran jam’iyyu, musamman a wasu jahohin da ke fama da rikicin siyasa na cikin gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara