DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Na bar PDP ne don cigaba da dangwalar arzikin da ke cikin kujerar da nake rike da ita – Shugaban majalisar dokokin jihar Edo

-

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Edo, Rt. Hon. Blessing Agbebaku, ya bayyana dalilin da ya sa ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.

Agbebaku, tare da wasu ‘yan majalisa biyu — Hon. Sunday Fada Eigbiremonlen da Hon. Idaiye Yekini Oisayemoje — sun sanar da sauya shekar su zuwa jam’iyyar APC a ranar Talata.

Google search engine

A yayin da yake sanar da wannan mataki a zauren majalisar a ranar Laraba, Agbebaku ya ce sauya shekar tasa ya samo asali ne daga niyyarsa ta ci gaba da rike kujerar shugaban majalisa domin amfanin mazabarsa.

Shugaban majalisar ya jaddada cewa sauya shekar ba don wani amfani na kai ba ne, illa dai kishin ci gaban al’umma da yankin da ya fito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ka fito ka bayyana wa ‘yan Nijeriya hakikanin dalilin da ya sa ka canza hafsoshin tsaro – Bukatar ADC ga shugaba Tinubu

Jam’iyyar ADC ta bukaci shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana gaskiya ga ’yan Nijeriya kan ainihin dalilan da suka sa aka yi gaggawar sauya shugabannin...

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya nada yayansa a matsayin Sarkin Duguri

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya naɗa yayansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sarkin sabon masarautar Duguri da aka ƙirƙira a jihar. Sakataren gwamnatin Jiha, Aminu...

Mafi Shahara