DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

-

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato NNPC.

Dangote ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa sabon shugaban rukunin NNPC, Injiniya Bayo Ojulari, a hedkwatar kamfanin da ke Abuja.

Google search engine

A wata sanarwa da mai magana da yawun NNPC, Olufemi Soneye, ya fitar a yau Jumma’a, Dangote ya ce akwai bukatar haɗin gwiwa domin tabbatar da samar da makamashi mai ɗorewa a ƙasar nan.

Ziyarar, a cewar Soneye, na cikin matakan da ake ɗauka domin ƙarfafa dangantaka da fahimtar juna tsakanin manyan kamfanonin mai biyu—na gwamnati da na masu zaman kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMMPRA Jaridar Daily Trust ta ce attajirin...

Nijeriya na bin kasashen Nijar, Togo da Benin tulin bashin kudin lantarkin da ya kai N25bn – NERC

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya NERC ta ce, kasar na bin kasashen Togo, Nijar da Benin bashin dala $17.8m — kimanin N25bn na lantarkin...

Mafi Shahara