DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

-

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu ‘yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da Hamid Mahmoud tsohon wakilin Muryar Amurka (VOA), da Maman Bachir Sani da kuma Masaouda Jaharou Sanda

Malan Anisse daya daya daga cikin shugabannin kafar ya shaida wa DCL cewa tun ranar Alhamis ne aka kama abokan aikin nasu, kuma har yanzu haka ana cigaba da tsare su a ofishin hukumar ‘yan sanda na jihar kafin a gabatar da su a gaban alkali.

Google search engine

An kama wadannan ‘yan jaridar ne dai sakamakon zargin su da bada labarin da ba gaskiya ba, kan cewa hukumomin kasar Nijar sun yanke hulda da hukumomin Rasha da na Turkiyya wanda suka ce su ma sun same shi ne daga wata kafa ta ketare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An dage jana’izar marigayi Muhammad Buhari zuwa ranar Talata -Dikko Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da shirye-shiryen jana'izar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga Yuli,...

Jam’iyyar ADC ta sanar da kwana uku na alhinin rashin tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari

Jam’iyyar ADC ta bayyana kwanaki uku na zaman makoki ga mambobinta don girmama marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi...

Mafi Shahara