DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yawan tarin jam’iyyu na lalata gwamnati, in ji Ganduje

-

Shugaban jam’iyyar APC ta kasa Abdullahi Umar Ganduje, ya ce babu laifi a yi tsarin jam’iyya daya idan har hakan ne ‘yan Nijeriya ke so.

Ganduje ya bayyana hakan ne bayan jagorantar Sanatoci uku na jam’iyyar PDP daga jihar Kebbi zuwa wata ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu a ranar Juma’a gabanin sauya shekar su zuwa jam’iyyar APC.

Google search engine

A cewar Ganduje, jam’iyyun siyasa da yawa suna lalata gwamnati.

Ya ce mafi yawan ‘yan jam’iyyun da suke dawowa jam’iyyar APC na komawa jam’iyyar saboda sunga kyakkyawan tsarin shugabanci da ke gudana a APC.

A cewarsa, kasar Sin tana daya daga cikin kasashe masu karfin fada aji a duniya, kuma tsarin jam’iyya daya ce suke amfani da shi dan haka ba abin kunya bane dan an yi tsarin jam’iyya daya a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara