DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin PDP sun kira taron kan sauyin sheka da jiga-jigan jam’iyyar ke yi

-

Gwamnonin jam’iyyar PDP za su yi taro a Abuja akan sauyin shekar da ‘yan jam’iyyar ke yi a kwanakinnan.

Wannan ya biyo bayan ficewar gwamnan jihar Delta Sheriff Oborevwori da Dr. Ifeanyi Okowa, da sauran ‘yan jam’iyyar PDP a jihar zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Gwamnonin sun gana makonni uku da suka gabata a Ibadan inda suka bayyana cewa jam’iyyar ba za su shiga tattaunawar hadaka da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar ke jagoranta ba.

Gwamnonin za su yi taron ne a gidan gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad da ke Asokoro a Abuja da nufin shawo kan matsalolin da suka dabaibaye jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP a Ondo ya fice daga jam’iyyar

Tsohon dan takarar gwamna a jihar Ondo Olugbenga Edema, na jam’iyyar NNPP, ya fice daga jam’iyyar. Edema ya mika wasikar barin jam'iyyar ga shugaban jam'iyyar na...

Sabbin hare-hare a kananan hukumomi hudu na jihar Benue sun yi ajalin mutum 23

Rahotanni na nuni da cewa kalla mutane 23 sun halaka a wasu jerin hare-haren da aka kai a wasu kananan hukumomi hudu na jihar Benue. Daily...

Mafi Shahara