Hukumomi a Nijeriya sun musanta rahoton da kungiyar Amnesty International ta fitar na yawan mutane dubu 10 da ‘yan bindiga suka yi ajali cikin shekaru 2 na mulkin Tinubu
Cibiyar yaki da ta’addanci ta kasa NCTC ta bayyana rahoton a matsayin mara inganci,inda ta bayyana cewa alkalumman Amnesty International ba su yi daidai da bayanan da gwamnati ke da shi ba.
A rahoton da Amnesty ta fitar ta ce kungiyoyin ‘yan bindiga da gungun masu aikata laifuka da ke dauke da makamai ne suka yi ajalin mutanen.
Sai dai hukumar ta NCTC ta gayyaci Amnesty domin ta fayyace mata bayanan da aka samu.



