DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lauyoyi sun maka sanatoci a kotu don neman a karbo wani kaso na albashinsu saboda gazawa a aiki

-

Wata kungiya mai suna Association of Legislative Drafting and Advocacy Practitioners (ALDRAP) ta shigar da kara a gaban Kotun Kare Hakkin Masu Sayayya, tana neman tilasta wa sanatocin Najeriya mayar da wani kaso mai yawa na albashinsu tun daga 2023, bisa zargin rashin tabuka abin kirki a majalisa.

Kungiyar a cewaar rahoton da jaridar Punch ta fitar tana neman a karbo cikakken albashin sanatoci 40 da suka rike kujeru a Majalisar Dattawa da kuma Majalisun ECOWAS da Afirka, wanda suka yi rufa-rufa a aiyukan mazabunsu.

Google search engine

A cewar sanarwar da sakataren gudanarwa na ALDRAP, Amuga Williams, ya aika wa shugaban majalisar, Godswill Akpabio a ranar 26 ga Mayu, hakkin ‘yan Nijeriya ne su ci gajiyar ayyukan mazabu daga majalissa, kuma sun dauki matakin ne a madadinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara