Ministan babban birnin tarayyar Nijeriya Abuja Nyesom Wike, ya bayyana cewa yana daga cikin wadanda suka taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da shaharar jam’iyyar PDP tare da kafa ta a matsayin babbar jam’iyya mai tasiri a matakin kasa da jihohi.
Wike ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta kai tsaye da ya yi da manema labarai a Abuja.
Yayin da yake martani ga suka da wani jigo a jam’iyyar PDP kuma mamba na kwamitin amintattu na jam’iyyar, Chief Bode George, ya yi dangane da rufe hedikwatar jam’iyyar ta kasa, Wike ya shawarci dattijon siyasar da ya zauna a gidansa ya ci gaba da karanta jaridu idan babu abin da yake yi.
Ya kara da bayyana cewa ba shi ko jam’iyyar za su iya biyan kudin haraji (ground rent) ba, domin kadarar ba a rubuta ta da sunan su ba.