DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba na bakin ciki da nasarar da PSG ta samu a gasar Champions League – Mbappe

-

Kyaftin din tawagar kwallon kafa ta Faransa, Kyllian Mbappe ya ce ko kadan bai yi bakin ciki da nasarar da tsohuwar kungiyarsa ta kwallon kafa PSG ta samu a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai wato Champion league ba.

Mbappe ya bayyana ma ‘yan jaridu gabanin wasan da za su buga a ranar Lahadi cewa, lokacin barinsa PSG ne ya yi ba wai ya yi gaggawar tafiya ba ne kuma ko kadan bai yi da-na-sani ba.

Google search engine

Nasarar PSG a Champions league ba tare da ni ba sam bai dame ni ba, ina murna da hakan don ina ganin sun cancanta.

Mbappe, mai shekaru 26 ya sauya sheka daga PSG zuwa Real Madrid a 2024 cike da fatar cin kofin Champions league, sai dai hakan bai yiwu ba sakamakon fitar da su da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta yi a watan Afrilu.

Idan ba a manta ba, PSG ta lallasa Inter Milan da ci 5-0 a wasan karshe na Champions league wanda shi ne Karin farko da kungiyar PSG ta ci kofin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara