DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna neman a yi wa marigayi DPO na Rano jihar Kano adalci – Wata kungiya

-

Kungiyar al’adu da ci-gaban kabilar Eggon, ta koka game da mummuna harin da ya kai ga rasa ran daya daga cikinsu wato, ASP Baba Mohammed, DPO din Rano.

Mohammed, dan asalin jihar Nasarawa, shi ne wanda wasu matasa suka far masa wanda hakan ya yi sanadiyar rasa ransa a Jihar Kano.

Google search engine

A cikin wani jawabi da kungiyar ta yi ma ‘yan jarida a garin Lafiya, Shugaban Kungiyar na kasa, Mandy Abuluya ya yi kira ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta yi bincike don gano wadanda suka aikata wannan barnar tare da hukunta su.

Mandy ya jajanta ma iyalan mamacin, da kuma kabilar Eggon, gwamnatin jihar da Shugaban ‘yan sandan Nijeriya game da lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin kaya zai sauka zuwa kashi ɗaya cikin goma – fadar shugaban Nijeriya

Fadar shugaban kasa ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa hauhawar farashin kaya (inflation) a kasar zai ci gaba da sauka, har ya kai zuwa kasa...

’Yan sanda sun kama mutanen da ake zargi da satar kifi a jihar Neja

Rundunar ’yan sandan jihar Neja ta sanar da kama mutane hudu bisa zargin sata da kuma karɓar kayan sata, bayan da aka sace kifaye da...

Mafi Shahara