DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna neman a yi wa marigayi DPO na Rano jihar Kano adalci – Wata kungiya

-

Kungiyar al’adu da ci-gaban kabilar Eggon, ta koka game da mummuna harin da ya kai ga rasa ran daya daga cikinsu wato, ASP Baba Mohammed, DPO din Rano.

Mohammed, dan asalin jihar Nasarawa, shi ne wanda wasu matasa suka far masa wanda hakan ya yi sanadiyar rasa ransa a Jihar Kano.

Google search engine

A cikin wani jawabi da kungiyar ta yi ma ‘yan jarida a garin Lafiya, Shugaban Kungiyar na kasa, Mandy Abuluya ya yi kira ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta yi bincike don gano wadanda suka aikata wannan barnar tare da hukunta su.

Mandy ya jajanta ma iyalan mamacin, da kuma kabilar Eggon, gwamnatin jihar da Shugaban ‘yan sandan Nijeriya game da lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara