A safiyar ranar Alhamis Kasshim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Adis Ababa domin ziyarar aiki bisa gayyatar da Firaministan kasar Dr Abiy Ahmed Ali ya yi masa.
A yayin ziyarar, zai shiga cikin sahun mutanen da za su kaddamar da shirin “Ethiopia Green Legacy”
Shirin wanda aka tsara shi domin yakar sare dazuzzuka, da kuma dakile illolin sauyin yanayi, an yi niyyar dasa bishiyu biliyan 20 cikin shekaru hudu masu zuwa.
Nijeriya da Ethiopia suna da tarihi tsakanin kasashen biyu, tare da yin hadin gwiwa a fannoni daban-daban, wanzar da zaman lafiya da kuma dangantakar tattalin arziki.