DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sandan jihar Katsina sun musanta labarin barayin daji sun karbe ikon karamar hukumar Kankara ta jihar

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta ce tana sane da wani labari da ta kira na karya da ake yadawa musamman a kafar sadarwar X cewa barayin daji sun karbe ikon yankin karamar hukumar Kankara ta jihar.

A cikin sanarwar da kakakin rundunar DSP Sadiq Abubakar Aliyu ya fitar, rundunar ‘yan sandan ta ce kwata-kwata babu kanshin gaskiya a labarin, an kirkiro shi ne kawai don a jefa tsoro a zukatan jama’a musamman na yankin karamar hukumar Kankara da sauran ‘yan jihar Katsina.

Google search engine

Rundunar ‘yan sandan ta bukaci mutane da su yi watsi da wadannan bayanai da ta kira na karya da ke yawo l. Sannan ta ba da tabbacin cewa tana nan tana bincike don zakulo waÉ—anda suka kitsa labarin don daukar matakin da ya dace a kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara