DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wani jami’in gwamnatin jihar Plateau da ya zo yi mana ta’aziyyar mutanenmu da aka yi ajalinsu – Sarkin Zazzau

-

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Amb Ahmed Nuhu Bamalli, ya nuna damuwarsa kan yadda babu wata tawagar jami’an gwamnati daga Jihar Plateau da ta zo Zaria domin yi wa iyalan waɗanda aka kashe a ƙaramar hukumar Mangu na jihar ta’aziyya.

An dai kashe mutanen ne a hanyar su ta zuwa ɗaurin aure daga jihar ta Plateau daga jihar Kaduna.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ruwaito yadda aka kai hari kan wasu matafiya su 31 da ke hanyarsu zuwa ɗaurin aure, inda wasu 13 suka rasa rayukansu, yayin da wasu suka jikkata, sannan aka ƙone motar da suke ciki kurmus.

Mai Martaba Sarkin ya bayyana haka ne yayin da yake karɓar tawagar shugabannin addinai ƙarƙashin jagorancin tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, a fadarsa da ke Zaria jihar Kaduna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara