Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba wai kawai tana gyara hanyoyi da ababen more rayuwa ba, har da dawo da yarda tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa.
Shettima wanda jaridar Punch ta ambato ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin kaddamar da gyaran titin da ya tashi daga Aguma Palace zuwa Radio Nigeria ya tsaya a New Market da ke karamar hukumar Gwagwalada a birnin tarayya Abuja, inda ya wakilci Shugaba Tinubu.
Ya ce zamanin alkawurra marasa tushe ya wuce, domin gwamnatin Tinubu na tabbatar da aiwatar da ayyukan da ta dauko da kuma gina yarda tsakanin gwamnati da al’umma.



