DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ko Seyi Tinubu aka nada shugaban hukumar zaben INEC, sai APC ta fadi a 2027 – Solomon Dalung

-

Tsohon Ministan Matasa da Cigaban Wasanni a Nijeriya, Solomon Dalung, ya bayyana cewa duk da wasu muhimman nade-nade ko dabarun siyasa, Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC za su sha kaye a babban zaben shekarar 2027.

Da yake magana a tashar talabijin ta News Central, Dalung ya yi watsi da tasirin sauya sheka ko nade-naden da Shugaba Tinubu ke yi, yana mai cewa ra’ayin jama’a ne zai yi rinjaye.

Google search engine

Ya kara da cewa ko da gwamnoni 36 suka koma APC, kuma ya nada Seyi Tinubu a matsayin shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, har ma ya nada matarsa a matsayin Babbar Alkalin Alkalan Nijeriya, kuma ko da INEC ce ta zama cibiyar karshe da ta sauya sheka zuwa APC, za su sha kaye a 2027.

Ya zargi gwamnatin Tinubu da kaddamar da yaki a kan al’ummar Nijeriya, yana mai nuna halin kuncin rayuwa da kuma abin da ya kira rashin adalci da gwamnati ke daukar nauyinsa.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara