DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisa ta gindaya sharuddan da Sanata Natasha za ta cika kafin a mayar da ita kan aiki bayan hukuncin kotu

-

Majalisar Dattawan Nijeriya ta gindaya wasu sharudda kafin ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kan kujerarta, bayan wata kotun tarayya da ke Abuja ta soke dakatarwar watanni shida da majalisar ta yi mata.

A hukuncin da ta yanke a ranar Juma’a, Mai shari’a Binta Nyako ta umurci Majalisar Dattawan da ta dawo da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, inda ta bayyana dakatarwar a matsayin mai tsanani da ya wuce kima.

Google search engine

Da yake mayar da martani kan hukuncin, mai magana da yawun Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce ba za a dawo da Sanata Natasha kai tsaye ba.

Adaramodu ya bayyana cewa hukuncin kotu bai soke ikon tsarin kundin tsarin mulkin da ke ba Majalisar Dattawa damar ladabtar da mambobinta ba.

Ya kara da cewa Majalisar za ta sake zama domin tattauna batun ne kawai bayan Akpoti-Uduaghan ta cika umarnin kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara