DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisa ta gindaya sharuddan da Sanata Natasha za ta cika kafin a mayar da ita kan aiki bayan hukuncin kotu

-

Majalisar Dattawan Nijeriya ta gindaya wasu sharudda kafin ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kan kujerarta, bayan wata kotun tarayya da ke Abuja ta soke dakatarwar watanni shida da majalisar ta yi mata.

A hukuncin da ta yanke a ranar Juma’a, Mai shari’a Binta Nyako ta umurci Majalisar Dattawan da ta dawo da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, inda ta bayyana dakatarwar a matsayin mai tsanani da ya wuce kima.

Google search engine

Da yake mayar da martani kan hukuncin, mai magana da yawun Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce ba za a dawo da Sanata Natasha kai tsaye ba.

Adaramodu ya bayyana cewa hukuncin kotu bai soke ikon tsarin kundin tsarin mulkin da ke ba Majalisar Dattawa damar ladabtar da mambobinta ba.

Ya kara da cewa Majalisar za ta sake zama domin tattauna batun ne kawai bayan Akpoti-Uduaghan ta cika umarnin kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara