DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Tinubu ya yi murabus

-

Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire na Najeriya Geoffrey Nnaji ya yi murabus daga mukaminsa biyo bayan cece-kuce kan zargin sa da yin amfani da takardun karatu na bogi.

Labari mai alaka: Sakataren gwamnatin Jihar Bauchi ya yi murabus daga mukaminsa

Google search engine

Nnaji, wanda aka nada a watan Agustan shekarar 2023, ya sanar da murabus din nasa ne a cikin wata wasika da ya aike wa Shugaban a ranar Talata, inda ya yi godiya bisa damar da aka ba shi ta yi wa kasa hidima.

Gabanin daukar wannan mataki, Nnaji ya ce akwai abokan hamayya a siyasa da ke ta yunkurin bata masa suna.

Labari mai alaka: An sallami daraktoci 33 daga aiki a ma’aikatar sufurin sama

Murabus din nasa ya zo ne a daidai lokacin da ake ta muhawara kan sahihancin takardun karatunsa daga Jami’ar Nsukka, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara