DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya ja layi da wanda ba sa goyon bayan Tinubu

-

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce zai mara wa duk dan takarar da ke goyon bayan Shugaban Kasa, Bola Tinubu, baya a zaben kananan hukumomin FCT da za a gudanar ranar 21 ga Fabrairu, 2026.

Wike ya bayyana hakan ne a birnin Abuja yayin bikin cika shekaru 60 na Sanata Sandy Onor, inda ya ce matsayinsa wajibi ne da ya rataya a wuyansa na goyon bayan shugaban kasa.

Google search engine

A cewar Hukumar zaben Nijeriya, INEC, kimanin masu kada kuri’a miliyan 1.68 ne aka tantance domin kada kuri’unsu a zaben.

Inda za a zabi shugabanni da mataimakansu a kananan hukumomi shida na FCT, tare da kansiloli 62 da za su wakilci mazabu 68.

Hukumar ta kuma tabbatar da amfani da manhajar IReV domin nuna sakamakon zabe kai tsaye don kara gaskiya a zabukan kasar.

Manyan jam’iyyun siyasa da suka hada da APC, PDP da ADC sun tsayar da ‘yan takararsu a zaben, yayin da wata babbar kotun tarayya ta hana jam’iyyar LP tsayar da ‘yan takara a zaben bisa zargin tangarda a tsarin fidda gwani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufai ya nemi Ribadu ya yi karin haske kan ‘gubar’ thallium sulphate mai matukar hatsari

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bukaci Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribadu, da ya fayyace rahotannin...

Hadin kan siyasa na karuwa a Kano – Gwaman Kano

Gwamnan Kano State, Abba Kabir Yusuf, ya ce ana samun ci gaba a hadin kan siyasa a jihar, yana mai fatan rikicin masarautar Kano zai...

Mafi Shahara