DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya rushe majalisar gudanarwa ta jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke jihar Anambra

-

Shugaba Tinubu

A cikin wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasar shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar ya ce rushe majalisar gudanarwar ya biyo bayan rahotannin da ke nuna cewa akwai wasu abubuwa da majalisar ke yi ba bisa ka’ida ba.

Google search engine

Gwamnatin ta nuna damuwarta kan yadda majalisar ta nuna rashin kula da dokokin jami’ar wajen zaben wasu shugabanni.

Sanarwar ta ce shugaba Tinubu ya kuma rushe shugabancin Engr. Ohieku Muhammed Salami a matsayin Pro-chancellor kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar tarayya ta kimiyar lafiya dake Otukpo a jihar Benue.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara