DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fada ya kaure tsakanin wasu direbobi da manajojin Dangote a Obajana

-

Wasu bayanai da DCL Hausa ta samu na cewa wani hargitsi ya kaure tsakanin wasu direbobin motocin kamfanin Dangote da ke kamfanin na Obajana a jihar Kogi da wasu manajojin kamfanin.
Majiyar DCL Hausa da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce rikicin har ya yi sanadiyyar ji wa wasu daga cikin manajojin raunuka munana.
“Da idona, na ga an karya manaja daya, amma wasu abokan aikina sun ce wadanda aka karya sun fi mutum daya”, in ji majiyar.
Wannan rikici dai na zuwa ne a daidai lokacin da direbobin motocin kamfanin na Dangote ke zargin akwai wasu daga cikin manajojin da ke yi musu kwange a wajen biyansu hakkokinsu, lamarin da ya yi sanadiyyar suka tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara