DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na ba kasashen Togo da Benin wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 24, in ji kamfanin TCN

-

Manajan Daraktan 
kamfanin rarraba wutar lantarki a Nijeriya Sule Abdul’aziz ya sanar cewa kasar na ba kasashe makwabta na Togo da Benin wutar lantarki ta sa’o’i 24 a duk rana.
Sule Abdul’aziz ya sanar da hakan a lokacin da yake jawabi a wani shirin gidan talabijin na Channels.
 Ya kara cewa Nijeriya na samar da lantarkin ga wadannan kasashe kuma suna biya yadda ya kamata. 
Sai dai ya ce ko a Nijeriya ma akwai masu samun wutar lantarki ta sa’o’i 24, musamman waÉ—anda ke saman tsarin Band A, suna samun ta sa’o’i 20-22, kama yadda jaridar Punch ta rawaito.
Kamfanin TCN dai ya ce an tsara ba waÉ—anda suke saman tsarin Band A, wutar lantarki ta sa’o’i 20-24, sai na saman Band B aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20, sai waÉ—anda ke saman tsarin Band C aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20 a rana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manufofin Tinubu ne ke jan hankalin ‘yan siyasa zuwa APC – Gwamnan Nassarawa

Gwamnan jihar Nassarawa Abdullahi Sule ya ce guguwar sauyin sheka tsakanin 'yan siyasa da ake samu a baya bayan nan musamman ga masu shiga APC,...

Dan majalisar wakilan Nijeriya daga Benue ya fice daga PDP zuwa APC

Dan majalisar wakilan Nijeriya mai wakiltar Apa/Agatu da ke jihar Benue, Ojoma Ojotu ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa APC. Bayanin sauya shekar dan...

Mafi Shahara