DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba Faransa ce ke ingiza ECOWAS daukar matakai kan Nijar ba – Ministan Tinubu

-

Ministan harkokin kasashen waje na Nijeriya Amb Yusuf Tuggar ya sanar cewa babu kanshin gaskiya a zargin da wasu ke yi cewa kasar Faransa ce ke ingiza kungiyar ECOWAS ta dauki matakan kakaba takunkumai ga kasar Nijar tun bayan juyin mulkin soji.
Kungiyar ECOWAS sai ta sanya wasu takunkumai ga kasar Nijar tun bayan da sojoji suka hambarar da gwamnatin farar hula ta Bazoum Mohammed a farko-farkon wannan shekara.
Daga cikin takunkuman akwai na rufe kan iyakar Nijeriya da Nijar da yanke wutar lantarki da katse huldar jakadanci da sauransu.
Ministan ya yi wannan furucin ne a wata zantawa da gidan talabijin na Trust Tv.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara