DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisa sun kori kwamishinan kasafin kudin daga zauren majalisar dokokin jihar Zamfara

-

‘Yan majalisar dokokin jihar Zamfara sun bukaci da kwamishinan kudi na jihar Abdulmalik Gajam da ya fita daga zauren majalisar a lokacin da Gwamna Dauda ya gabatar musu da daftarin kasafin kudin 2024.
‘Yan majalisar dai sun ce sun dauki wannan matakin ne biyo bayan kin mutunta gayyatar majalisar da suka ce kwamishinan ya yi, na ya je gabansu don kare kasafin kudin shekarar 2024.
Bayan tattaunawa, majalisar ta amince cewa takardar tabbatarwar da ta ba kwamishinan tun da farko, ta janye.
Kamar yadda suka ce, sun gayyaci kwamishinan sau uku don ya je majalisar ya kare kasafin kudin shekarar 2024 na ma’aikatarsa, amma ya ki zuwa, kuma bai bayar da wata hujja mai kwari ba.
Bayan kammala bayyana wadannan dalilai na su, ‘yan majalisar sun bukaci kwamishinan da ya fita daga zauren majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara