DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An damfari ‘yan Nijeriya sama da 1,000 da sunan za a ba su aiki a Ingila – IOM

-

Hukumar da ke kula da masu gudun hijira ta majalisar dinkin duniya IOM ta ce akwai ‘yan Nijeriya sama da dubu daya da aka damfara da sunan za a samar musu aiki a kasar Ingila.
Babban jami’in hukumar a Nijeriya Laurent De Boeck ya sanar da hakan a Abuja a lokacin da yake ganawa da manema labarai.
Mr Boeck ya ce kusan kowanensu ya yi asarar kudin da suka kai darajar Dala dubu 10,000 ta dalilin neman aikin, amma ba a yi kwado da yaro ba kuma ba a bashi gayansa ba.
Mr Laurent ya ce idan suka je ma’aikatun suka gabatar da takardun kama aikin da aka damfare su aka ba su, sai ma’aikatun su ce wannan takarda ba daga gare su take ba.
Ya ce da yawansu suna can sun yi tsuru-tsuru a Ingila ba su da kudin komowa Nijeriya, a yayin da wasu kuma ke kunyar dawowa su tunkari iyalansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sojojin Amurka na jiran umarnin Trump don kai farmaki Nijeriya

Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar da shirin kai farmaki a Nijeriya bayan umarnin tsohon shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, bisa zargin...

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Mafi Shahara