DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An damfari ‘yan Nijeriya sama da 1,000 da sunan za a ba su aiki a Ingila – IOM

-

Hukumar da ke kula da masu gudun hijira ta majalisar dinkin duniya IOM ta ce akwai ‘yan Nijeriya sama da dubu daya da aka damfara da sunan za a samar musu aiki a kasar Ingila.
Babban jami’in hukumar a Nijeriya Laurent De Boeck ya sanar da hakan a Abuja a lokacin da yake ganawa da manema labarai.
Mr Boeck ya ce kusan kowanensu ya yi asarar kudin da suka kai darajar Dala dubu 10,000 ta dalilin neman aikin, amma ba a yi kwado da yaro ba kuma ba a bashi gayansa ba.
Mr Laurent ya ce idan suka je ma’aikatun suka gabatar da takardun kama aikin da aka damfare su aka ba su, sai ma’aikatun su ce wannan takarda ba daga gare su take ba.
Ya ce da yawansu suna can sun yi tsuru-tsuru a Ingila ba su da kudin komowa Nijeriya, a yayin da wasu kuma ke kunyar dawowa su tunkari iyalansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara