DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC na zawarcin Wike

-

Jam’iyyar APC ta ce tana nan tana zawarcin tsohon Gwamnan Rivers kuma ministan Abuja a halin yanzu Mr Nyesom Wike zuwa jam’iyyar.
Jam’iyyar ta ce muddin ya karbi tayinta na komawa, zai zama shi ne babban jigo kuma jagoranta a jihar Rivers.
Jaridar Daily Trust ta ba da labarin cewa Wike na yawan nanata cewa shi dan jam’iyyar PDP ne duk kuwa tarnaki da ciwon kan da ake ganin ya ba PDP bayan ya fadi zaben fitar da gwani a zaben shekarar 2023 da Atiku Abubakar ya kayar da shi.
A baya-bayan nan, baraka ta kunno kai tsakanin Wike da yaronsa a siyasa Gwamnan Rivers na yanzu Sim Fubara da hakan ya jaza tsagewar majalisar dokokin jihar gida biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara