DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku Abubakar ya musanta karbar tallafin kudin kamfe daga Gwamna Sanwo Olu na jihar Lagos a lokacin zaben 2023

-

Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar musanta ikirarin da ake na cewa gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya bashi tallafin kudi na yakin neman zabe a zaben shugaban kasa da ya gabata.

Google search engine

A wata sanarwa da mai magana da yawun sa Paul Ibe ya fitar, ofishin yada labarai na Atiku ya karyata rahotannin da ke nuni da cewa Sanwo-Olu, ta hannun Ms. Aisha Achimugu, ya bai wa tsohon mataimakin shugaban kasa kudi da ake zargin mallakar jihar Legas ne, abinda ya kira makircin ‘yan siyasa da suka kulla.

A farkon makon da ya gabata ne jaridar PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa ana binciken Ms Achimugu kan zargin karkatar da kudade da dama.

Hukumar EFCC mai yaki da cin hani da rashawa a Nijeriya na ci gaba da binciken matar da ake zargi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara