DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya sanar da soke hawan Sallah

-

Alhaji Aminu Ado Bayero 

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke hawan Sallah da aka saba yi duk shekara, kamar yadda aka tsara gudanarwa a baya.

Sarkin ya bayyana hakan ne, a cikin wani takaitaccen faifan bidiyo da ya fitar a daren Laraba, inda ya bayyana dalilan da suka sanya aka dakatar da shirin hawan Sallar.

Google search engine

Ta cikin faifan bidiyon, sarki Aminu, ya bayyana cewa ya bada umarnin soke hawan ne sakamakon kokarin da malaman addinin musulunci da kuma dattawa suka yi wajen ganin an samu zaman lafiya, inda ya bukaci mazauna birnin Kano da su yi amfani da lokacin bikin Sallar wajen ziyartar yan uwa da abokan arziki tare da samun damar halartar bikin Sallah.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

CDD ta horas da ‘yan jarida a Katsina kan yaki da labaran karya

Cibiyar bunkasa dimokradiyya ta CDD ta horas da ‘yan jarida a jihar Katsina kan aiki mai inganci. CDD ta ce wannan na a wani yunkuri na...

‘Yan bindiga sun halaka mutum 1,sun kuma mutane 5 a Zamfara

’Yan bindiga sun kai hari kauyen Fananawa da ke karamar hukumar Bukuyum ta jihar Zamfara, inda suka halaka mutum ɗaya tare da sace mutane biyar,...

Mafi Shahara