DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An ji karar harbe-harbe a wurin taron magoya bayan Wike a jihar Bayelsa

-

An shiga cikin tashin hankali a birnin Yenagoa ta jihar Bayelsa, bisa karar harbe-harbe da aka ji a wurin masu biyayya ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike karkashin wata kungiya mai suna NEW Associates.

Kungiyar ta shirya taron ne karkashin jagorancin George Turnah, jigo a jam’iyyar PDP a jihar.

Google search engine

Ana ci gaba da gudanar da taron ne a lokacin da aka yi ta jin karar harbe-harbe a yankin, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.

Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan harbe-harbe, sakataren kungiyar NEW Associates a jihar Bayelsa, Comrade Ebilade Ekerefe, ya ce za su ci gaba da gudanar da taron.

A halin yanzu, magoya bayan NEW Associates sun sake haduwa don ci gaba da gangamin taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban kasar Djibouti zai sake tsayawa takara karo na shida

Shugaban ƙasar Djibouti mai shekaru 77, Ismail Omar Guelleh zai sake tsayawa takara karo na shida Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh, wanda yake mulki tun...

Dan takarar ADC a zaben gwamnan Anambara ya zargi jam’iyyar APGA da sayen kuri’u

Dan takarar ADC a zaben gwamnan Anambra, John Nwosu, ya zargi jam’iyyar APGA da sayan da kuri’a a zaben da yake ci-gaba da gudana a...

Mafi Shahara