DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Nasir Idris na Kebbi ya nesanta kansa daga jita-jitar ficewa daga jam’iyyar APC

-

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya nesanta kansa daga rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa shi da wasu gwamnoni hudu na shirin ficewa daga jam’iyyar APC don shiga wata hadaka da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da wasu ‘yan siyasa ke kokarin kafawa.

Google search engine

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ahmed Idris, ya fitar, Gwamna Idris ya bayyana rahotannin a matsayin karya, da kuma kage, inda ya tabbatar da cewa shi ba dan siyasa ne mai yawo daga jam’iyya zuwa jam’iyya ba.

Gwamnan ya ce “Ina da tushe a APC, ‘jam’iyyar APC ce ta daga ni, kuma ina wa APC hidima,” yana mai jaddada cewa ko da kowa zai fice a jam’iyyar APC, shi ne zai zama na karshe da zai bar jam’iyyar da ta gina shi.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara