DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwalejojin ilimi na tarayya za su fara ba da shahadar digirin farko a Nijeriya – Gwamnatin Tarayya

-

Gwamnatin Nijeriya ta ce ta fara aiwatar da tsarin karatu a dukkan kwalejojin ilimi na tarayya, wanda zai bai wa kwalejojin damar ba da takardar shedar malanta a Nijeriya da kuma Digiri na farko a fannin ilimi.

Wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar ilimi ta tarayya Folasade Boriowo ya fitar, ya ce wannan ya biyo bayan dokar kwalejojin ilimin tarayya ta 2023 da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa hannu.

Google search engine

Da yake kaddamar da tsarin a Abuja, Ministan Ilimi Dokta Tunji Alausa ya nuni da cewa wannan gagarumin ci gaba ne da zai sake fasalin ilimin a Nijeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara