DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwalejojin ilimi na tarayya za su fara ba da shahadar digirin farko a Nijeriya – Gwamnatin Tarayya

-

Gwamnatin Nijeriya ta ce ta fara aiwatar da tsarin karatu a dukkan kwalejojin ilimi na tarayya, wanda zai bai wa kwalejojin damar ba da takardar shedar malanta a Nijeriya da kuma Digiri na farko a fannin ilimi.

Wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar ilimi ta tarayya Folasade Boriowo ya fitar, ya ce wannan ya biyo bayan dokar kwalejojin ilimin tarayya ta 2023 da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa hannu.

Google search engine

Da yake kaddamar da tsarin a Abuja, Ministan Ilimi Dokta Tunji Alausa ya nuni da cewa wannan gagarumin ci gaba ne da zai sake fasalin ilimin a Nijeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

NNPP ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya ta wanke Kwankwaso daga zargin tallafa wa ta’addanci

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya da Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA) su fito su wanke jagoranta na...

Kotu a Kano ta daure jarumar Kannywood Samha Inuwa watanni 6 a gidan gyaran hali

Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Mai shari’a S.M. Shuaibu, ya yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa wadda aka fi sani da Samha,...

Mafi Shahara