Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Nijeriya ta bukaci sabon shugaban hukumar kula da gidajen gyaran hali...

Gwamnatin Nijeriya ta bukaci sabon shugaban hukumar kula da gidajen gyaran hali ya mayar da hankali wajen sauya tunanin daurarru

Gwamnatin tarayya ta bukaci sabon shugaban hukumar kula da gidajen ajiya da gyaran hali na kasar Sylvester Nwakuchi, da ya mayar da hankali wajen sauya tunani da kuma rayuwar daurarru maimakon hukunta su kawai.

Ministan harkokin cikin gida Dr. Olubunmi Tunji Ojo ne ya yi wannan kira yayin bikin nadin da aka yi wa sabon shugaban hukumar a birnin Abuja, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A jawabinsa, ministan ya jaddada muhimmancin shugabanci na gari ta hanyar rikon gaskiya da amana wajen kawo sauyi mai inganci a tsarin gidajen ajiya da gyaran hali, tare da dora wa sabon shugaban alhakin tabbatar da sauyi cikin watanni 19 masu zuwa.

A nasa bangaren, Sylvester Nwakuchi ya yi godiya da sabon mukamin naa tare da bayyana shirin sa na inganta tsaro, rage cinkoso, samar da gine gine da kuma walwalar ma’aikata.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata